Wildebeest analysis examples for:   hau-hausa   ’    February 11, 2023 at 18:42    Script wb_pprint_html.py   by Ulf Hermjakob

2  GEN 1:2  To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe koina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
11  GEN 1:11  Saan nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da yaya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
12  GEN 1:12  Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da yaya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da yaya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
26  GEN 1:26  Saan nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
29  GEN 1:29  Saan nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da yaya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da yaya, don su zama abinci a gare ku.
35  GEN 2:4  Wannan shi ne asalin tarihin sammai da duniya saad da aka halicce su. Saad da Ubangiji Allah ya yi duniya da sammai,
37  GEN 2:6  amma dai rafuffuka suna ɓullo da ruwa daga ƙasa suna jiƙe koina a fāɗin ƙasa.
38  GEN 2:7  Saan nan Ubangiji Allah ya yi mutum daga turɓayar ƙasa, ya kuma hura numfashin rai cikin hancinsa, mutumin kuwa ya zama rayayyen taliki.
47  GEN 2:16  Ubangiji Allah ya umarci mutumin ya ce, “Kana da yanci ka ci daga kowane itace a cikin lambun,
53  GEN 2:22  Saan nan Ubangiji Allah ya yi mace daga haƙarƙarin da ya ɗauko daga mutumin, ya kuwa kawo ta wurin mutumin.
54  GEN 2:23  Sai mutumin ya ce, “Yanzu kam wannan ƙashi ne na ƙasusuwana nama kuma na namana. Za a ce da ita ‘mace, gama an ciro ta daga namiji.”
57  GEN 3:1  To, maciji dai ya fi kowane a cikin namun jejin da Ubangiji Allah ya yi wayo. Ya ce wa macen, “Tabbatacce ne Allah ya ce, ‘Kada ku ci daga kowane itace a lambu?”
58  GEN 3:2  Macen ta ce wa macijin, “Za mu iya ci daga yaya itatuwa a lambun,
59  GEN 3:3  amma Allah ya ce, ‘Kada ku ci daga yayan itacen da yake tsakiyar lambu, kada kuma ku taɓa shi, in ba haka ba kuwa za ku mutu.
61  GEN 3:5  Gama Allah ya san cewa saad da kuka ci daga itacen idanunku za su buɗe, za ku kuma zama kamar Allah, ku san abin da yake mai kyau da abin da yake mugu.”
62  GEN 3:6  Saad da macen ta ga yayan itacen suna da kyau don abinci, abin shaawa ga ido, abin marmari kuma don samun hikima, sai ta tsinka ta ci, ta kuma ba da waɗansu wa mijinta wanda yake tare da ita, shi ma ya ci.
63  GEN 3:7  Saan nan idanun dukansu biyu suka buɗe, suka kuma gane tsirara suke; saboda haka suka ɗinɗinka ganyayen ɓaure suka yi wa kansu sutura.
68  GEN 3:12  Mutumin ya ce, “Macen da ka sa a nan tare da ni, ita ta ba ni waɗansu yaya daga itacen, na kuwa ci.”
70  GEN 3:14  Saboda haka Ubangiji Allah ya ce wa macijin, “Saboda ka yi haka, “Na laanta ka cikin dukan dabbobi da kuma cikin dukan namun jeji! Daga yanzu rubda ciki za ka yi tafiya turɓaya kuma za ka ci dukan kwanakin rayuwarka.
72  GEN 3:16  Saan nan ya ce wa macen, “Zan tsananta naƙudarki ainun, da azaba kuma za ki haifi yaya. Za ki riƙa yin marmarin mijinki zai kuwa yi mulki a kanki.”
73  GEN 3:17  Ga Adamu kuwa ya ce, “Saboda ka saurari matarka, ka kuma ci daga itacen da na ce, ‘Kada ka ci, “Za a laanta ƙasa saboda kai. Da wahala za ka ci daga cikinta dukan kwanakin rayuwarka.
76  GEN 3:20  Mutumin ya sa wa matarsa suna, Hawwau, gama za tă zama mahaifiyar masu rai duka.
77  GEN 3:21  Ubangiji Allah ya yi tufafin fata domin Adamu da Hawwau, ya kuma yi musu sutura.
81  GEN 4:1  Adamu ya kwana da matarsa Hawwau, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
82  GEN 4:2  Daga baya ta haifi ɗanuwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Saad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
84  GEN 4:4  Amma Habila ya kawo mafi kyau daga yayan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
88  GEN 4:8  To, Kayinu ya ce wa ɗanuwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
89  GEN 4:9  Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗanuwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗanuwana ne?”
90  GEN 4:10  Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗanuwanka yana mini kuka daga ƙasa.
91  GEN 4:11  Yanzu, kai laananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗanuwanka daga hannunka.
95  GEN 4:15  Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Saan nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
101  GEN 4:21  Sunan ɗanuwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
102  GEN 4:22  Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe. Yaruwar Tubal-Kayinu ita ce Naama.
104  GEN 4:24  Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau sabain da bakwai ke nan.”
107  GEN 5:1  Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Saad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
108  GEN 5:2  Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Saad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
109  GEN 5:3  Saad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
110  GEN 5:4  Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu yaya maza da mata.
111  GEN 5:5  Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, saan nan ya mutu.
112  GEN 5:6  Saad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
113  GEN 5:7  Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu yaya maza da mata.
114  GEN 5:8  Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, saan nan ya mutu.
115  GEN 5:9  Saad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
116  GEN 5:10  Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu yaya maza da mata.
117  GEN 5:11  Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, saan nan ya mutu.
118  GEN 5:12  Saad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
119  GEN 5:13  Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu yaya maza da mata
120  GEN 5:14  Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, saan nan ya mutu.
121  GEN 5:15  Saad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
122  GEN 5:16  Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu yaya maza da mata
123  GEN 5:17  Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, saan nan ya mutu.
124  GEN 5:18  Saad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
125  GEN 5:19  Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu yaya maza da mata.
126  GEN 5:20  Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, saan nan ya mutu.
127  GEN 5:21  Saad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
128  GEN 5:22  Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu yaya maza da mata.
130  GEN 5:24  Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, saan nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
131  GEN 5:25  Saad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
132  GEN 5:26  Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu yaya maza da mata.
133  GEN 5:27  Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, saan nan ya mutu.
134  GEN 5:28  Saad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
135  GEN 5:29  Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana taaziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya laanta.”
136  GEN 5:30  Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da yaya maza da mata.
137  GEN 5:31  Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, saan nan ya mutu.
139  GEN 6:1  Saad da mutane suka fara ƙaruwa a duniya, aka kuma hahhaifi musu yaya mata,
140  GEN 6:2  sai yayan Allah maza suka ga cewa yayan mutane mata suna da banshaawa, sai suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura.
141  GEN 6:3  Saan nan Ubangiji ya ce, “Ruhuna ba zai zauna a cikin mutum har abada ba, saboda shi mai mutuwa ne, kwanakinsa za su zama shekaru ɗari da arbain ne.”
142  GEN 6:4  Nefilimawa suna nan a duniya a waɗancan kwanaki, da kuma kwanakin da suka bi baya, a saad da yayan Allah suka kwana da yayan mutane mata, suka kuma hahhaifi musu yaya. Ai, su ne jarumawan dā, mutanen da suka shahara.
148  GEN 6:10  Nuhu yana da yaya maza uku, Shem, Ham da Yafet.
156  GEN 6:18  Amma zan kafa alkawarina da kai, kai kuma za ka shiga jirgin, kai da yayanka maza da matarka da matan yayanka tare da kai.
161  GEN 7:1  Saan nan Ubangiji ya ce wa Nuhu. “Shiga jirgin, kai da dukan iyalinka, gama na ga kai mai adalci ne a wannan zamani.
164  GEN 7:4  Kwana bakwai daga yanzu zan aiko da ruwa a duniya yini arbain da dare arbain, zan kuma kawar da kowace halitta mai rai da na yi daga doron ƙasa.”
166  GEN 7:6  Nuhu yana da shekaru 106 ne saad da aka yi ambaliya ruwa a duniya.
167  GEN 7:7  Nuhu da matarsa da yayansa da matansu, suka shiga jirgi domin su tsira daga ruwa ambaliya.
172  GEN 7:12  Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya, yini arbain da dare arbain.
173  GEN 7:13  A wannan rana Nuhu tare da matarsa da yayansa maza, Shem, Ham da Yafet da matansu uku suka shiga jirgi.
176  GEN 7:16  Dabbobi da kowane abu mai rai da suka shiga ciki, namiji ne da ta mace, yadda Allah ya umarci Nuhu. Saan nan Ubangiji ya kulle jirgin daga baya.
177  GEN 7:17  Kwana arbain ambaliya ta yi ta saukowa a duniya, saad da ruwa ya yi ta ƙaruwa sai ya yi ta ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can bisa duniya.
190  GEN 8:6  Bayan kwana arbain, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
195  GEN 8:11  Saad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Saan nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
199  GEN 8:15  Saan nan Allah ya ce wa Nuhu,
200  GEN 8:16  “Fito daga jirgin, kai da matarka da yayanka maza da matansu.
202  GEN 8:18  Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da yayansa maza da matan yayansa,
205  GEN 8:21  Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara laanta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
207  GEN 9:1  Saan nan Allah ya sa wa Nuhu da yayansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi yaya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
211  GEN 9:5  Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗanuwansa.
214  GEN 9:8  Sai Allah ya ce wa Nuhu da yayansa,
220  GEN 9:14  Duk saad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
222  GEN 9:16  Duk saad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
224  GEN 9:18  Yayan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kanana.)
225  GEN 9:19  Waɗannan su ne yayan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
227  GEN 9:21  Saad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
228  GEN 9:22  Ham, mahaifin Kanana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa yanuwansa biyu a waje.
229  GEN 9:23  Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, saan nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
230  GEN 9:24  Saad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
231  GEN 9:25  sai ya ce, “Kanana laananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga yanuwansa.”
232  GEN 9:26  Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kanana yă zama bawan Shem.
233  GEN 9:27  Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kanana yă zama bawansa.”
235  GEN 9:29  Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, saan nan ya mutu.
236  GEN 10:1  Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet, yayan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi yaya maza bayan ambaliyar.