39 | GEN 2:8 | To, fa, Ubangiji Allah ya yi lambu a gabas, a Eden, a can kuwa ya sa mutumin da ya yi. |
41 | GEN 2:10 | Akwai wani kogi mai ba da ruwa ga lambun wanda ya gangaro daga Eden, daga nan ya rarrabu, ya zama koguna huɗu. |
46 | GEN 2:15 | Ubangiji Allah ya ɗauko mutumin ya sa shi cikin Lambun Eden domin yă nome shi, yă kuma lura da shi. |
79 | GEN 3:23 | Saboda haka Ubangiji Allah ya kore shi daga Lambun Eden domin yă nome ƙasa wadda aka yi shi. |
80 | GEN 3:24 | Bayan da ya kori mutumin, sai ya sa kerubobi da takobi mai harshen wuta yana jujjuyawa baya da gaba a gabashin Lambun Eden don yă tsare hanya zuwa itacen rai. |
96 | GEN 4:16 | Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden. |
97 | GEN 4:17 | Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok. |
98 | GEN 4:18 | Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek. |
106 | GEN 4:26 | Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji. |
112 | GEN 5:6 | Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh. |
113 | GEN 5:7 | Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata. |
115 | GEN 5:9 | Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan. |
116 | GEN 5:10 | Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata. |
117 | GEN 5:11 | Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu. |
124 | GEN 5:18 | Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok. |
125 | GEN 5:19 | Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata. |
127 | GEN 5:21 | Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela. |
128 | GEN 5:22 | Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata. |
129 | GEN 5:23 | Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365. |
130 | GEN 5:24 | Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi. |
239 | GEN 10:4 | ’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim. |
245 | GEN 10:10 | Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar. |
256 | GEN 10:21 | Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet, ’ya’ya maza. Shem shi ne kakan ’ya’yan Eber duka. |
257 | GEN 10:22 | ’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram. |
259 | GEN 10:24 | Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber. |
260 | GEN 10:25 | Aka haifa wa Eber ’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan. |
281 | GEN 11:14 | Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber. |
282 | GEN 11:15 | Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata. |
283 | GEN 11:16 | Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg. |
284 | GEN 11:17 | Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu ’ya’ya maza da mata. |
338 | GEN 14:1 | A zamanin Amrafel sarkin Shinar, shi da Ariyok sarkin Ellasar, Kedorlayomer sarkin Elam, da kuma Tidal sarkin Goyim |
342 | GEN 14:5 | A shekara ta goma sha huɗu, Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi suka tafi suka cinye Refahiyawa a Ashterot Karnayim, Zuziyawa a Ham, Emawa a Shabe Kiriyatayim, |
343 | GEN 14:6 | da Horiyawa a ƙasar tudun Seyir har zuwa El Faran kusa da hamada. |
344 | GEN 14:7 | Sa’an nan suka juya suka tafi En Mishfat (wato, Kadesh), suka cinye dukan ƙasar Amalekawa, da kuma Amoriyawa waɗanda suke zaune a Hazazon Tamar. |
346 | GEN 14:9 | gāba da Kedorlayomer sarkin Elam, Tidal sarkin Goyim, Amrafel sarkin Shinar da Ariyok sarkin Ellasar; sarakuna huɗu gāba da biyar. |
350 | GEN 14:13 | Sai wani wanda ya tsira, ya zo ya faɗa wa Abram mutumin Ibraniyawa. Abram kuwa yana zama kusa da manyan itatuwan Mamre, Mamre mutumin Amoriyawa ne ɗan’uwan Eshkol da Aner, su kuwa abokan Abram ne. |
361 | GEN 14:24 | Ba zan karɓi kome ba, sai dai abin da mutanena suka ci da kuma rabon mutanen da suka tafi tare da ni, ga Aner, Eshkol, da Mamre. Bari su ɗauki rabonsu.” |
363 | GEN 15:2 | Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?” |
580 | GEN 23:8 | Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina |
582 | GEN 23:10 | Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni. |
585 | GEN 23:13 | ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.” |
586 | GEN 23:14 | Efron ya ce wa Ibrahim, |
588 | GEN 23:16 | Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da ’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin. |
589 | GEN 23:17 | Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka |
663 | GEN 25:4 | ’Ya’yan Midiyan maza su ne, Efa, Efer, Hanok, Abida, da kuma Elda’a. Dukan waɗannan zuriyar Ketura ce. |
668 | GEN 25:9 | ’Ya’yansa maza kuwa Ishaku da Ishmayel suka binne shi cikin kogon Makfela, kusa da Mamre, a cikin filin Efron ɗan Zohar mutumin Hitti, |
689 | GEN 25:30 | Ya ce wa Yaƙub, “Ina roƙonka, ka ɗan ɗiba mini faten nan! Ina fama da yunwa!” (Shi ya sa aka kira shi Edom.) |
713 | GEN 26:20 | Amma makiyayan Gerar suka yi faɗa da na Ishaku suka ce, “Ruwan namu ne!” Saboda haka Ishaku ya ba wa rijiyar suna Esek, domin sun yi faɗa da shi. |
727 | GEN 26:34 | Sa’ad da Yaƙub ya kai shekaru arba’in da haihuwa, sai ya auri Yudit ’yar Beyeri mutumin Hitti, da kuma Basemat ’yar Elon mutumin Hitti. |
932 | GEN 32:4 | Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom. |
981 | GEN 33:20 | A can ya kafa bagade ya kuma kira shi El Elohe Isra’ila. |
1019 | GEN 35:7 | A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa. |
1028 | GEN 35:16 | Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai. |
1031 | GEN 35:19 | Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem). |
1033 | GEN 35:21 | Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder. |
1042 | GEN 36:1 | Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom). |
1043 | GEN 36:2 | Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada ’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama ’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye |
1045 | GEN 36:4 | Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel. |
1049 | GEN 36:8 | Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir. |
1050 | GEN 36:9 | Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir. |
1051 | GEN 36:10 | Waɗannan su ne sunayen ’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa. |
1052 | GEN 36:11 | ’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz. |
1053 | GEN 36:12 | Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa. |
1056 | GEN 36:15 | Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa, ’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz, |
1057 | GEN 36:16 | Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada. |
1058 | GEN 36:17 | ’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa. |
1060 | GEN 36:19 | Waɗannan su ne ’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu. |
1062 | GEN 36:21 | Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, ’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom. |
1064 | GEN 36:23 | ’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam. |
1067 | GEN 36:26 | ’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran. |
1068 | GEN 36:27 | ’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan. |
1071 | GEN 36:30 | Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir. |
1072 | GEN 36:31 | Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki, |
1073 | GEN 36:32 | Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba. |
1082 | GEN 36:41 | Oholibama, Ela, Finon. |
1084 | GEN 36:43 | Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom. |
1123 | GEN 38:3 | ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa, wanda aka kira Er. |
1126 | GEN 38:6 | Sai Yahuda ya auro wa Er mata, ɗansa na fari, sunanta Tamar. |
1127 | GEN 38:7 | Amma Er, ɗan farin Yahuda mugu ne a fuskar Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi. |
1134 | GEN 38:14 | sai ta tuɓe rigunan gwaurancinta ta rufe kanta da lulluɓi don ta ɓad da kamanninta, sa’an nan ta je ta zauna a ƙofar shigar Enayim, wadda take a hanyar zuwa Timna. Gama ta lura cewa ko da yake Shela yanzu ya yi girma, ba a ba da ita gare shi ta zama matarsa ba. |
1141 | GEN 38:21 | Ya tambayi mutanen da suke zama a can ya ce, “Ina karuwar haikalin da take a bakin hanya a Enayim?” Sai suka ce, “Ba a taɓa kasance da karuwar haikali a nan ba.” |
1248 | GEN 41:52 | Ya ba wa ɗansa na biyu suna Efraim ya ce, “Gama Allah ya wadata ni cikin wahalata.” |
1399 | GEN 46:12 | ’Ya’yan Yahuda maza su ne, Er, Onan, Shela, Ferez da Zera (amma Er da Onan sun mutu a ƙasar Kan’ana). ’Ya’yan Ferez maza su ne, Hezron da Hamul. |
1401 | GEN 46:14 | ’Ya’yan Zebulun maza su ne, Sered, Elon da Yaleyel. |
1403 | GEN 46:16 | ’Ya’yan Gad maza su ne, Zafon, Haggi, Shuni, Ezbon, Eri, Arodi da Areli. |
1407 | GEN 46:20 | A Masar, Asenat ’yar Fotifera, firist na On ta haifi Manasse da Efraim wa Yusuf. |
1408 | GEN 46:21 | ’Ya’yan Benyamin maza su ne, Bela, Beker, Ashbel, Gera, Na’aman, Ehi, Rosh, Muffim, Huffim da Ard. |
1453 | GEN 48:1 | Bayan wani lokaci aka faɗa wa Yusuf, “Mahaifinka yana ciwo.” Sai ya ɗauki ’ya’yansa maza biyu, Manasse da Efraim suka tafi tare da shi. |
1457 | GEN 48:5 | “To, yanzu, ’ya’ya mazanka biyu da aka haifa maka a Masar kafin in zo a nan za su zama nawa; Efraim da Manasse za su zama nawa, kamar yadda Ruben da Simeyon suke nawa. |
1459 | GEN 48:7 | Yayinda nake dawowa daga Faddan Aram, cikin baƙin cikina Rahila ta rasu a ƙasar Kan’ana yayinda muke kan hanya, ’yar rata daga Efrata. Saboda haka na binne ta a can kusa da hanya zuwa Efrata” (wato, Betlehem). |
1465 | GEN 48:13 | Yusuf ya ɗauke su biyu, Efraim a damansa zuwa hagun Isra’ila, Manasse kuma a hagunsa zuwa hannun daman Isra’ila, ya kuma kawo su kusa da shi. |
1466 | GEN 48:14 | Amma Isra’ila ya miƙa hannun damansa ya sa shi a kan Efraim, ko da yake shi ne ƙaramin, ta wurin harɗewa hannuwansa, ya sa hannun hagunsa a kan Manasse, ko da yake Manasse ne ɗan farinsa. |