Wildebeest analysis examples for:   hau-hausa   a    February 11, 2023 at 18:42    Script wb_pprint_html.py   by Ulf Hermjakob

1  GEN 1:1  A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
2  GEN 1:2  To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
3  GEN 1:3  Sai Allah ya ce, “Bari haske kasance,” sai kuwa ga haske.
4  GEN 1:4  Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
5  GEN 1:5  Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
6  GEN 1:6  Allah ya ce, “Bari sarari kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
7  GEN 1:7  Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙaashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
8  GEN 1:8  Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
9  GEN 1:9  Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙaashin sama tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa bayyana.” Haka kuwa ya kasance.